Mai Martaba Sarkin Kano mai murabus Muhammadu Sunusi na II ya ja kunnen jama’a kan kar su zabi duk wanda ya ce gyara kasar nan abune mai sauki.
A cewarsa duk wanda ya ce gyaran kasar nan abune mai sauki to ya yi “karya”.
Muhammadu Sunusi na wadannan kalamai ne yayin taron zuba jari da Gwamnatin Kaduna ta shirya ranar Asabar.
Ya ce matakan da za a dauka na gyaran Najeriya ba za su yi dadi ba