Kotun daukaka kara a Kano ta bada umarnin a sake gurfanar da dan takarar gwamnan Kano Abdulkarim A Zaura bisa zargin damfara.
Idan za a iya tunawa dai wata babbar kotun jihar Kano ce ta wanke A A Zauran daga dukkanin tuhume-tuhumen da ake masa.
Hukumar EFCC ce ta gurfanar da shi kan zarge zarge 5 a gaban babbar kotun tarayya dake Kano.
Hukumar ta zargi shi da damfarar wani dan kasar Kuwait kudi har Dala Miliyan 1 da dubu dari uku da 20 bisa batun cewa yana harkallar gina gidaje a Dubai da Kuwait da sauran kasashen larabawa.
A ranar 9 ga watan Yuni na shekarar 2020, mai shari’a Lewis Allagoa ya wanke A A Zaura daga zargin.
Sai dai lauyan masu kara ya daukaka kara kan hukuncin.
A hukuncin kotun daukaka karar mai alkalai 3 ta yi watsi da hukuncin babbar kotun Inda ta yi umarni a sake gurfanar da shi a gaban wata kotun.