Saurari premier Radio
24.5 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiDamfara:Kotu ta bada umarnin sake gurfanar da A A Zaura

Damfara:Kotu ta bada umarnin sake gurfanar da A A Zaura

Date:

Kotun daukaka kara a Kano ta bada umarnin a sake gurfanar da dan takarar gwamnan Kano Abdulkarim A Zaura bisa zargin damfara.

Idan za a iya tunawa dai wata babbar kotun jihar Kano ce ta wanke A A Zauran daga dukkanin tuhume-tuhumen da ake masa.

Hukumar EFCC ce ta gurfanar da shi kan zarge zarge 5 a gaban babbar kotun tarayya dake Kano.

Hukumar ta zargi shi da damfarar wani dan kasar Kuwait kudi har Dala Miliyan 1 da dubu dari uku da 20 bisa batun cewa yana harkallar gina gidaje a Dubai da Kuwait da sauran kasashen larabawa.

A ranar 9 ga watan Yuni na shekarar 2020, mai shari’a Lewis Allagoa ya wanke A A Zaura daga zargin.

Sai dai lauyan masu kara ya daukaka kara kan hukuncin.

A hukuncin kotun daukaka karar mai alkalai 3 ta yi watsi da hukuncin babbar kotun Inda ta yi umarni a sake gurfanar da shi a gaban wata kotun.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...