Saurari premier Radio
38.9 C
Kano
Wednesday, April 24, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiDaliban Kano dubu 15 na cikin barazanar rasa jarrabawar NECO

Daliban Kano dubu 15 na cikin barazanar rasa jarrabawar NECO

Date:

Ahmad Hamisu Gwale

Akalla daliban Kano dubu goma 15 ka iya rasa rubuta jarrabawar NECO da ake shirin fara gudanarwa a ranar Litinin dinnan 27 ga Yunin da muke ciki.

Tuni hukumar shirya jarrabawar NECO ta kammala shirin fara gudanar da jarrabawar a dukanin jihohin kasar nan daga ranar Litiinin mai zuwa.

Daliban Kano kimanin dubu 15 ne ka iya fuskantar gaza rubuta jarrabawar, biyo bayan kudin da NECO ta bayyana tana bin gwamnatin Kano har kimanin Biliyan daya da dubu dari biyar.

A zantawar wakilin Premier Radio Ahmad Hamisu Gwale da masanin ilimin zamantakewar dan Adam Dakta Idris Salisu Rogo Malami ne a jami’ar Bayero dake Kano yace lamarin abin takaici ne kuma zai iya kawowa ilimin jihar nakasu.

‘Matuka akwai takaici yadda aka samu jinkirin biyan kudin da NECO kebin gwamnatin Kano, wanda kuma lamarin zai sanya jihar ta kara samun koma baya a ci gaban ilimin jihar’, a cewar Idris Salisu Rogo.

Koda muka tuntubi Sakatariya a hukumar Ilimi ta jihar Kano wadda Hajiya Lauratu Ado Diso ke jagoranta bamu samu ji daga gare taba, sakamakon kin shiga da wayar ta takiyi.

Kuma a gefe guda mun aika mata da sakon karta kwana, amma har kawo yanzu bata bada amsar sakon da muka aike mat aba.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...