Umar Idris Shuaibu
Rundunar tsaro ta Civil Defence ta kama wasu ma’aurata biyu bisa zargin dukan kawo wuka da suka yiwa ‘yar aikin su.
Yarinyar mai suna Nana Sha’una Yusuf mai shekaru 14, ta dade tana shan azaban a hannun iyayen gidan nata.
A cewar rundunar iyayen gidan nata su ne Ahmad Abdulkarim da Safiyya Shamsuddeen da ke zaune a Unguwar Na’ibawa ‘yan Katako.
Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Ibrahim Idris Abdullahi ya aikewa Premier Radio.
Binciken da rundunar Civil Defence ta gudanar na nuni da cewa magidantan sun rika azabatar da Nana har sai da bayanta ya cika da alamun tabo na duka.
A yazu haka yarinyar wadda yar asalin Kazauren Jijar Jigawa ce na ci gaba da samun kulawar jami’an lafiya tun bayan da rundunar tsaron Civil Defence ta kama ma’auratan.
Rundunar ta kara da cewa, tuni wadanda ake zargin da tursasa ‘yar aikin su kan abubuwan da basu kamace ta ba, da cin zali aka gurfanar da su gaban kotu bayan amsa laifin su da suka yi.