Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Saturday, April 20, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiAddiniBa a nada Sarkin Sharifai na kasa idan ba daga Kano ya...

Ba a nada Sarkin Sharifai na kasa idan ba daga Kano ya ke ba – Zuri’ar Almaghili

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Masarautar sharifai ta kasa da ke da shalkwatarta a Kano ta koka kan yadda wasu da ke kiran kansu sharifai suke amfanin da sunan wajen barace-barace da neman mulki.

Babban wakilin masarautar Sharifai ta kasa karkashin zuri’ar Sheikh Salihu Almagili Sharif Abdulkarim Sahrif Ali ne ya yi wannan korafi yayin taron maneman labarai a Kano.

Sharif Abdulkarim ya ce abin takaici ne a samu wasu na kokarin cusa kansu cikin shugabancin sahrifai na kasa bayan ba su gada ba, har ma su yi ikirarin cewar su ke jan ragamar sharfai a kasar nan.

Ya kara da cewa shekara da shekaru zuri’ar Sheikh Salihu Almaghili  ke jagorancin Sharifai a kasar nan kuma tun wancan lokaci har yanzu ba a sauyaba.

Sai dai wani abu da ya ja hankalinsu shi ne yadda suka ji wani mutum ya fito daga jihar Zamfara da ke ikiran shi ne sarkin Sharifai na kasa.

A cewarsa wannan ya saba ka’idar yadda ake nada shugabancin sharifai a kasar nan.

Sharif Abdulkarim ya kara da cewa wanda ke ikirarin kansa sarkin sharifai na kasa na yin amfani da damar kasancewarsa Sharifi ne kawai yana damfarar al’umma.

Har ma aka jiyo shi ya ziyarci gwamnan Zamfara ya kuma nada shi garkuwan sharifan, da a cewarsa wannan duk wani salo ne na damfara.

Ba a sarkin sharifai ba a zuri’ar Almaghili ba.

Sharu Abdulkarin ya ce a yadda aka san sarautar Sharifai dole ne arkin sharifa ya zama ya fito da ga tsatson Almagili, haka kuma fadar sarkin sahrifai na kasa ta kasance a unguwar sharifai Zauren Tudu da ke nan Kano.

Amma saboda son abin duniya da kuma kawo wargi cikin al’amarin ya sanya wasu ke ikirarin sarautar Sharifai, su ke kuma tafiya neman kudi da ita.

A don hakan ne ya ja hankalin jama’a da masu madafun iko su dinga tantance suwaye sharifai na gaskiya da kuma na bogi.

Masu madafan iko su dinga tantancewa kafin hukunci

 Sahrifin ya ci ga ba da cewa akwai bukatar masu mukamai da ake zuwa musu da irin wannan damfara su dinga bin diddigin duk mutumin da ya zo musu da sunan sarautar sharifa.

A cewarsa galibin masu zuwa wurinsu da sunan sarautar sharifai na zuwa ne kawai domin neman na abinci.

Ya kuma ce tuni suka fara bin diddigin inda matsalar ta samo asali har wani daga jihar Zamfara ya ke kiran kansa da sarkin sharifai, kuma za su dauki matakin gaggawa.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...