Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiAddiniAn nada Sheikh Nuru Khalid sabon limamin Juma'a a Abuja

An nada Sheikh Nuru Khalid sabon limamin Juma’a a Abuja

Date:

Mukhtar Yahya Usman
Sabon Masallacin Juma’a da ke unguwar bayan babban bankin kasa CBN ya nada sheikh Nuru Khalid babban limamin Masallacin.

Wannan na zuwa ne awannin kadan bayan da kwamitin Masallacin Juma’a na APO ya Kori Malamin baki daya.

Kwamitin Masallacin ya zargi Malamin da gudanar da hudubar da za ta tada hankulan jama’a.

A cewar shugaban kwamitin Masallacin Sanata Dan Sadau, sun kori Malamin ne saboda kin nuna nadamarsa bayan da aka dakatar da shi.

Sai dai jim kadan bayan korar tasa ne malamin ya samu sabon aiki da Masallacin da ke unguwar babban bankin kasa CBN.

Ana sa ran zai kama aiki a ranar Juma’a mai zuwa 8 ga Aprilu, Inda zai jagoranco Sallar Juma’a.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...