Saurari premier Radio
29.9 C
Kano
Friday, April 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiAn fara daukar sunayen malaman dake zuwa aiki a jami'ar Sule Lamido...

An fara daukar sunayen malaman dake zuwa aiki a jami’ar Sule Lamido dake Jigawa

Date:

Muhammad Bello Dabai

 

Jami’ar Sule Lamido dake Kafin Hausa a jihar Jigawa ta umarci malaman dake koyarwa a jami’ar da su koma bakin aiki.

 

Wannan matakin na zuwane bayan taron gaggawa da hukumar gudanarwar jami’ar ta gudanar karo na 30.

 

A sanarwar da sakataren jami’ar Malam Adamu Mohammed ya fitar, tace tuni jami’ar ta umarci shugabannin sassanta da fara daukar sunayen malaman da suka koma aiki daga jiya litinin zuwa 5 ga watan gobe.

 

Wannan mataki da jami’ar ta dauka baya rasa nasaba da gaza cimma matsaya tsakanin kungiyar malaman jami’o’i ta kasa ASUU da gwamnatin tarayya kan yajin aiki da aka kwashe sama da rabin shekara anayi.

 

To sai dai ana ganin akwai kalubale da jami’o’in na gwamnatocin jihohi zasu iya fuskanta, duba da akwai malaman jami’o’i mallakin gwamnatin tarayya masu yawa da sune suke koyarwa a jami’o’in mallakin jihohi

Latest stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...