Saurari premier Radio
23.4 C
Kano
Sunday, September 8, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiMataimakin shugaban kasar Kashim Shettima zai bar Najeriya a wannan Laraba domin...

Mataimakin shugaban kasar Kashim Shettima zai bar Najeriya a wannan Laraba domin wakiltar shugaba Bola Tinubu a taron shugabannin kasashen G77 a birnin Havana na kasar Cuba, wanda zai gudana daga ranar 15 zuwa 17 ga watan Satumba.

Date:

Mataimakin shugaban kasar Kashim Shettima zai bar Najeriya a wannan Laraba domin wakiltar shugaba Bola Tinubu a taron shugabannin kasashen G77 a birnin Havana na kasar Cuba, wanda zai gudana daga ranar 15 zuwa 17 ga watan Satumba.
Daraktan yada labarai na ofishin mataimakin shugaban kasa, Olusola Abiola, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce Shettima zai bi sahun sauran shugabannin duniya ciki har da babban sakataren majalisar Dinkin Duniya Antonio Gutteres a wajen taron.
Ya ce taron zai tattauna batutuwan ci gaban da mambobin kungiyar ke fuskanta, musamman daga kudancin duniya.
Taken taron shi ne Kalubalen Ci gaba na Yanzu: Matsayin Kimiyya, Fasaha da Ƙirƙira.
Najeriya ta kasance daga cikin mambobin da suka kafa kungiyar G77 da kasashe masu tasowa 77 suka kafa a shekarar 1964.
Kashim Shettima zai samu rakiyar ministan noma da raya karkara Abubakar Kyari, da takwaransa na kere-kere, kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, da kuma babban sakataren ma’aikatar harkokin waje, Mista Adamu Lamuwa

Latest stories

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye muƙaminsa

Mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan...

Related stories

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye muƙaminsa

Mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan...