Najeriya ta rasa matakin farko na kasashen Nahiyar Afirka da su ka fi samar da man A yanzu.
Libya ta karbe matakin farko yayin da Angola ta kasance na biyu a jerin kasashe mafi samar da mai.
Najeriya na daga cikin kasashen da ke ba da gudunmawa wurin samar da mai a duniya duba da tarun arzikin kasar na mai.
Nahiyar Afirka na ba da gudunmawar fiye da kaso 8 na mai a duniya, amma farkon 2023, an samu matsaloli da dama.
Rahoton Energy Chamber ya ce daga watan Janairu zuwa Mayu Nahiyar ta yi asarar fiye da gangan mai dubu 180 a ko wace rana.
Najeriya ta rasa matakin farko a Nahiyar wacce ta fi kowa kasa samar da mai bayan samun matsalolo masu tarin yawa da su ka hada da satar mai din musamman a jihohin Kudu maso Kudu.
Kasar ta fado har mataki na uku bayan Libya da Angola sun karbe matakin farko da na biyu a Nahiyar a matsayin mafi samar da man.
Kasar nan dai ta yi asarar fiye da gangan mai dubu 165 a rana cikin watanni biyar na farkon shekarar 2023.
Najeriya ta rasa matakin farko na kasashen Nahiyar Afirka da su ka fi samar da man A yanzu.
Date: