Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ,zata fafata da Manchester City a wasan karshe na gasar cin kofin kalubale na kasar Ingila FA Cup.
Wannan dai na zuwa ne bayan da Man United tayi nasarar doke Brighton da ci 7-6 a bugun daga kai sai mai tsaran gida a ranar Lahadi.
Ita kuwa Man City tin a ranar Asabar ta lallasa Shefield United da ci 3-0 a wasan da suka fafata.
Yanzu haka dai a karon farko a wasan karshe a gasar FA Cup, Man City da Man United zasu kece raini da juna a gasar ta kakar wasannin shekarar 2022/2023.
Kuma ana saran wasan karshen zai gudana a ranar Uku ga watan Yunin bana, kuma babban filin wasan kasar Ingila Wembley ne zai karbi bakuncin wasan.