Saurari premier Radio
23.4 C
Kano
Sunday, September 8, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiWasanniFA Cup:Man City da Man United zasu kece raini da juna a...

FA Cup:Man City da Man United zasu kece raini da juna a wasan karshe

Date:

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ,zata fafata da Manchester City a wasan karshe na gasar cin kofin kalubale na kasar Ingila FA Cup.

Wannan dai na zuwa ne bayan da Man United tayi nasarar doke Brighton da ci 7-6 a bugun daga kai sai mai tsaran gida a ranar Lahadi.

Ita kuwa Man City tin a ranar Asabar ta lallasa Shefield United da ci 3-0 a wasan da suka fafata.

Yanzu haka dai a karon farko a wasan karshe a gasar FA Cup, Man City da Man United zasu kece raini da juna a gasar ta kakar wasannin shekarar 2022/2023.

Kuma ana saran wasan karshen zai gudana a ranar Uku ga watan Yunin bana, kuma babban filin wasan kasar Ingila Wembley ne zai karbi bakuncin wasan.

Latest stories

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye muƙaminsa

Mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan...

Related stories

Sabbin Yan Wasa 12 da Kano Pillars ta dauka

Kungiyar kwallon Kafa ta Kano Pillars, wadda ta lashe...