Saurari premier Radio
23.4 C
Kano
Sunday, September 8, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiMatan Kano sun karrama Atiku Abubakar da Ludayi

Matan Kano sun karrama Atiku Abubakar da Ludayi

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Matan jam’iyyar PDP a Kano karkashin jagorancin sanata Baraka Sani sun karrama Alhaji Atiku Abubakar da katon ludayi.

 

A jawabinta sanata Baraka ta ce sun karrama shi da Ludayin da suka yiwa lakabi da na ‘Diban Romon Demokradiyya’ ne saboda cancantarsa.

 

Baraka ta ce mata su ne kashin bayan Demokradiyya don haka dole ne suma a basu damarsu don a dama da su.

 

Ya kuma bukaci dukkanin matan da ke jihar Kano su fito kwansu da kwarkwata domin su zabi Atiku Abubakar a matsayin shugaban kasa shekara mai zuwa.

 

Ta ce matan Kano ba za su yi nadama ko da na sani ba idan suka zabeshi.

 

A nasa jawabin Alhaji Atiku Abubakar ya godewa matan da suka taru don karramashi.

 

Ya ce ko Kadan ba zai basu kunya ba kuma zai Sanya bukatunsu a gaba da zarar ya zama shugaban kasa.

Latest stories

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye muƙaminsa

Mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan...

Related stories

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye muƙaminsa

Mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan...