Mutane biyu aka jikkata bayan da yan ta’adda suka farmaki jerin gwanon motocin shugaban Kasa Muhammadu Buhari, a cewar fadar shugaban kasa.
A daren jiya ne dai wasu yan ta’adda suka farmaki motocin a garin Dutsenma a hanyarsu ta zuwa Daura daga Abuja don tarar shugaban Kasa Muhammadu Buhari.
Fadar shugaban kasar ta tsara cewar shugaba Buhari zai yi sallar idi ne a garin Daura mahaifarsa.
Cikin wata sanarwa da kakakinsa Garba Shehu ya fitar ya ce mutane biyu ne sukaji rauni yayin harin.
Ya ce tuni aka garzaya da su Asibiti a ke kuma basu kulawa ta musamman.
Haka kuma fadar shugaban kasar ta nuna rashin Jin dadinta kan wannan hari.