Wani gini mai hawa bakwai da ba a kammala ba ya rushe a birnin Legas na inda ya ritsa da mutane da dama.
Rahotanni na cewa ginin, wanda ke kan Titin Oba Idowu Oniru, ya ritsa da mutum kusan shida bayan faÉ—owarsa a cikin dare wayewar garin Lahadi.
Sakataren hukumar agajin gaggawa reshen Jihar Legas, Dr Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce tuni suka ƙaddamar da aikin ceton waɗanda ginin ya rufe.
“Zuwanmu wurin ke da wuya muka tarar ginin mai hawa bakwai da ba a kammala ba ya rikito,” a cewarsa.
“Babu rahoton ko wani ya ji rauni amma ana zaton É“araguzai sun rufe mutum shida.”
Ya Æ™ara da cewa ma’aikatansu na buÆ™atar “manyan kayan aiki” a yunÆ™urin ceto mutanen.
Ya ce sun Æ™addamar da “shirin aikin ceto na gaggawa na Jihar Legas”.
A makon da ya gabata ma wani gini mai hawa uku ya faɗo a kasuwar sayar da wayoyi ta Beirut a nan Kano, wanda ya jawo asarar rayuka.