Saurari premier Radio
41.9 C
Kano
Friday, April 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiYan Kwankwasiyya sun mamaye babban zaben NNPP a Kano

Yan Kwankwasiyya sun mamaye babban zaben NNPP a Kano

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Dubban yan Kwankwasiyya ne suka mamaye harabar wurin da Jam’iyyar NNPP Mai kayan marmari za ta gudanar da baban zabenta.

An dai tsara gudanar da zaben ne a cibiyar koyar da Sana’o’i ta sani Abacha wato Abacha Youth Center da ke kan hayar Madobi.

Ana sa ran Jam’iyyar za ta zabi shugabaninta a mataki daban daban ayau Litinin.

Sai dai abinda ke jan hankali a wurin taron shi ne yadda magoya bayan Kwankwasiyya suka mamaye wurin.

Wannan dai baya rasa nasaba da yadda ake ta rade-radin jagoran Kwnkwasiyyar Rabiu Musa zai koma cikin Jam’iyyar.

Idan za a iya tunawa dai tun a watan da ya gabata ne Jam’iyyar ta rushe shugabancinta, tare da kafa kwamitin riko.

A yau Litinin ne dai aka tsara gudanar da zaben shugabannin Jam’iyyar da kuma ake ganin yan Kwnkwasiyya ne suka mamaye dukkanin mukaman da za zaba.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...