Tsohon gwamnan Legas kuma jagoran jam’iyyar APC Bola Ahmed Tinubu ya faɗawa matasan ƙasar nan cewa za su yi shugabancin ƙasa amma sai bayan ya yi.
Tinibu ya faɗi haka ne a ziyarar da ya kai wa Alaafin na Oyo Lamidi Adeyemi, a ranar Lahadi.
“Kun toshe wa magabatanku dama tun kafin ku zama shugaban ƙasa, idan kun zama shugaban ƙasa fa, za ku kore mu ne a gari?”
“Sai kun tsufa za ku zama shugaban ƙasa, kuma sai na riga zama shugaban ƙasa,” in ji Tinubu.
Matasa a Najeriya sun daɗe suna fafutikar ganin sun kai ga madafan iko, da samun muƙaman siyasa.