Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, zai wakilci Najeriya yayin jana’izar marigayiya Sarauniya Elizabeth ll ta kasar Ingila.
Sarauniya Elizabeth ll ta rasu a ranar 8 ga watan Satumba a gidan ta na shakatawa na Balmoral dake Scotland ita ce sarauniyar da ta fi dadewa a kan sarautar Burtaniya.
Osinbajo zai bar Abuja ne a yau Asabar don halartar Jana’izar da zata haɗa da dangin sarauta, da shugabannin kasashen duniya ciki har da mambobin kungiyar Commonwealth, firaministan kasashe,da aka shirya gudanarwa a Westminster Abbey dake birnin Landan a ranar Litinin.
Gabanin Jana’izar mataimakin shugaban kasar zai kasance cikin manyan baki da Sarki Charles lll da Sarauniya Camilla za su tarbe su, a wata liyafar da za a gabatar a fadar Buckingham, ranar Lahadi, a cewar wata sanarwa da sai magana da yawun mataimakin shugaban kasar Laolu Akande ya fitar.