Saurari premier Radio
33.9 C
Kano
Friday, April 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiNBC ta janye rufe wasu kafofin yada labarai a kasar nan

NBC ta janye rufe wasu kafofin yada labarai a kasar nan

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Hukumar Kula da Kafofin Yada Labarai ta kasa (NBC) ta janye dakatarwar da ta yi wa wasu kafofin yada labarai saboda gaza sabunta lasisinsu.

Darakta Janar na Hukumar, Malam Balarabe Shehu Ilelah ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Juma’a a Abuja.

Idan za a iya tunawa a ranar Juma’a, 19 ga watan Agustan 2022 ne NBC ta sanar da kwace lasisin kafofin yada labarai sama da 50.

Cikinsu kuwa har da kafar sadarwa ta Kamfanin DAAR da Rhythm FM da gidan talabijin na Silverbird , saboda bashin da take bin su na sama da Naira biliyan 2.6.

Matakin ya jawo suka ga hukumar wadda a kwanan nan ta ci tarar kafar labarai ta Media Trust naira miliyan biyar da wasu kamfanonin tauraron dan Adam kan fim din da suka haska game da ‘yan fashin daji a Jihar Zamfara.

Ilelah ya ce ya samu kyakkyawan martani daga tashoshin yada labaran da ba su sabunta lasisin nasu ba, wanda ya hada da manyan kafofin yada labarai cikin kasar.

“Bayan tattaunawa da jagororin kungiyar masu kafofin yada labarai da kuma sauran masu ruwa da tsaki a bangaren, mun dauki matakin dakatar da bukatar rufe wasu gidajen labaran a fadin kasar.” in ji Ilelah.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...