Ministan shari’a na kasa Lateef Fagbemi ya ce yajin aikin da ƙungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC suka fara a yau ya saɓa wa doka.
Yace kungiyoyin basu bi ka’idojin da dokar ƙwadago ta gindaya ba, kamar yadda tashar talabijin ta Channels ta ruwaito.
Ƙungiyoyin ƙwadagon na son a sanya albashi mafi ƙanƙanta kan naira dubu 494, yayinda gwamnati ta toke kan naira dubu 60.
A gefe guda wakilan NLC da TUC sun rufe hanyar shiga babban ofishin kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) da ke Abuja.
Yanzu haka dai ana cikin hali na rashin tabbas kan tasirin da yajin aikin zai yi, sai dai ana fargabar zai iya tsayar da al’amura a faɗin ƙasar.