Mata da dama ne suka mamayen Kofar majalisar kasar nan biyo bayan watsi da aka yi da bukatunsu jiya Talata a zauren Majalisar.
A jiya ne ‘yan majalisar suka fara kaɗa ƙuri’a kan wasu ƙudirori da aka gabatar na gyaran kundin tsarin mulki, ciki har da wanda ya nemi a bai wa matan kashi 35 cikin 100 na muƙaman siyasa.
Sai dai amma ‘yan majalisar sun yi watsi da kudirin.
![Abuja](https://ichef.bbci.co.uk/live-experience/cps/240/cpsprodpb/vivo/live/images/2022/3/2/e990ea93-5736-4eef-813a-a98485d7aee0.jpg 240w, https://ichef.bbci.co.uk/live-experience/cps/320/cpsprodpb/vivo/live/images/2022/3/2/e990ea93-5736-4eef-813a-a98485d7aee0.jpg 320w, https://ichef.bbci.co.uk/live-experience/cps/400/cpsprodpb/vivo/live/images/2022/3/2/e990ea93-5736-4eef-813a-a98485d7aee0.jpg 400w, https://ichef.bbci.co.uk/live-experience/cps/480/cpsprodpb/vivo/live/images/2022/3/2/e990ea93-5736-4eef-813a-a98485d7aee0.jpg 480w, https://ichef.bbci.co.uk/live-experience/cps/512/cpsprodpb/vivo/live/images/2022/3/2/e990ea93-5736-4eef-813a-a98485d7aee0.jpg 512w, https://ichef.bbci.co.uk/live-experience/cps/624/cpsprodpb/vivo/live/images/2022/3/2/e990ea93-5736-4eef-813a-a98485d7aee0.jpg 624w)
Matan da suka taru ƙarƙashin ƙungiyoyi daban-daban, sun ce zaman dirshan za su yi a bakin ƙofar.
“Ba za mu bar wajen nan ba har sai mun ga shugaban majalisa, sai majalisa ta bai wa mata ‘yancinsu,” a cewar Niri Goyit daga ƙungiyar Action Aid.
Lamarin ya faru duk da cewa Matar Shugaban Ƙasa Aisha Buhari ta je majalisar da kanta a makon da ya gabata don ganewa idonta da kuma tabbatar da cewa ƙudirorin mata sun samu karɓuwa a gyaran kundin tsarin mulkin.
A yau Laraba ne ‘yan majalisar za su kammala kaɗa ƙuri’a kan batutuwa kusan 60 da suka shafi gyaran ɓangarori daban-daban na kundin mulkin.