24.9 C
Kano
Sunday, June 4, 2023
HomeLabaraiMata sun yi zanga-zangar Allah-wadai da hana su mukaman siyasa a Abuja

Mata sun yi zanga-zangar Allah-wadai da hana su mukaman siyasa a Abuja

Date:

Related stories

Maniyyata 17,000 ne suka bar Najeriya zuwa kasa maitsarki-NAHCON

Bayan kwashe kwanaki bakwai da fara jigilar alhazan Najeriya...

Mata da dama ne suka mamayen Kofar majalisar kasar nan biyo bayan watsi da aka yi da bukatunsu jiya Talata a zauren Majalisar.

A jiya ne ‘yan majalisar suka fara kaɗa ƙuri’a kan wasu ƙudirori da aka gabatar na gyaran kundin tsarin mulki, ciki har da wanda ya nemi a bai wa matan kashi 35 cikin 100 na muƙaman siyasa.

Sai dai amma ‘yan majalisar sun yi watsi da kudirin.

Abuja

Matan da suka taru ƙarƙashin ƙungiyoyi daban-daban, sun ce zaman dirshan za su yi a bakin ƙofar.

“Ba za mu bar wajen nan ba har sai mun ga shugaban majalisa, sai majalisa ta bai wa mata ‘yancinsu,” a cewar Niri Goyit daga ƙungiyar Action Aid.

Lamarin ya faru duk da cewa Matar Shugaban Ƙasa Aisha Buhari ta je majalisar da kanta a makon da ya gabata don ganewa idonta da kuma tabbatar da cewa ƙudirorin mata sun samu karɓuwa a gyaran kundin tsarin mulkin.

A yau Laraba ne ‘yan majalisar za su kammala kaɗa ƙuri’a kan batutuwa kusan 60 da suka shafi gyaran ɓangarori daban-daban na kundin mulkin.

Latest stories