Saurari premier Radio
24.5 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiMata sun yi zanga-zangar Allah-wadai da hana su mukaman siyasa a Abuja

Mata sun yi zanga-zangar Allah-wadai da hana su mukaman siyasa a Abuja

Date:

Mata da dama ne suka mamayen Kofar majalisar kasar nan biyo bayan watsi da aka yi da bukatunsu jiya Talata a zauren Majalisar.

A jiya ne ‘yan majalisar suka fara kaɗa ƙuri’a kan wasu ƙudirori da aka gabatar na gyaran kundin tsarin mulki, ciki har da wanda ya nemi a bai wa matan kashi 35 cikin 100 na muƙaman siyasa.

Sai dai amma ‘yan majalisar sun yi watsi da kudirin.

Abuja

Matan da suka taru ƙarƙashin ƙungiyoyi daban-daban, sun ce zaman dirshan za su yi a bakin ƙofar.

“Ba za mu bar wajen nan ba har sai mun ga shugaban majalisa, sai majalisa ta bai wa mata ‘yancinsu,” a cewar Niri Goyit daga ƙungiyar Action Aid.

Lamarin ya faru duk da cewa Matar Shugaban Ƙasa Aisha Buhari ta je majalisar da kanta a makon da ya gabata don ganewa idonta da kuma tabbatar da cewa ƙudirorin mata sun samu karɓuwa a gyaran kundin tsarin mulkin.

A yau Laraba ne ‘yan majalisar za su kammala kaɗa ƙuri’a kan batutuwa kusan 60 da suka shafi gyaran ɓangarori daban-daban na kundin mulkin.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...