Saurari premier Radio
25.1 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiMai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi kira ga Gwamnatoci...

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi kira ga Gwamnatoci da Mawadata su fito su tallafawa marasa karfi a cikin al’uma

Date:

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi kira ga Gwamnatoci da Mawadata su fito su tallafawa marasa karfi a cikin al’uma.

Sarkin yayi wannan kira ne a wata hira da yayi da yan jaridu a fadarsa dangane da bikin ranar Agaji ta duniya.

Yace a matsayinsu na Shugabani kuma wadanda suke tare da talawa kuma suke sauraron koke kokensu a kullum ya zama wajibi su kara jan hankalin wadanda suke da wadata su dinga tallafawa makontansu wadanda basu dashi.
Sorkin

A gefe guda kuwa sarkin yayi bayanin cewa koda a kwanankin baya ya bayyanawa shugaban kasa halin da al’umma suke ciki na matsin rayuwa a wani zana da shugaban kasar yayi da Sarakunan kasar nan.

A bangaren hidintawa ga kungiyar agaji kuwa Sarkin yace kimanin shekaru talatin (30) kenan yana bayar da gudunmawa a kungiyar Agaji ta Jama’atu Nasrul Islam ta kasa.

Alhaji Aminu ado Bayero yace ya zagaya dukkanin lungu da Sako na kasar nan domin gudanar da aikin hidamtawa al’umma a kungiyar bayar da agaji ta Jama’atu Nasrul Islam a matsayinsa na shugaba.

mai martaba sarkin Alhaji Aminu Ado Bayero yayi bayanin cewar kungiyar bayar da Agajin ta samo asali ne tun zamanin Annabi Muhammad SAW,
Inda ya bayyana agaji da cewar tushensa shine addinin musulunci

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...