Fadar Shugaban Ƙasa ta yi watsi da ikirarin tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, cewa Najeriya ta samu ribar Naira tiriliyan 7 da biliyan dari 9 da 80 sakamakon hauhawar farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya.
A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar, Fadar Shugaban Ƙasa ta ce ƙididdigar Atiku ba ta yi la’akari da muhimman abubuwa da ke tasiri wajen lissafin kuɗaɗen shiga daga man fetur ba.
Sanarwar ta bayyana cewa an yi watsi da batutuwa kamar raguwar yawan ɗanyen man da Najeriya ke hakowa, kuɗaɗen samar da mai, da kuma yarjejeniyoyin sayar da ɗanyen mai da aka ƙulla tun kafin hauhawar farashin.
Haka kuma, ta jaddada cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziki da suka haɗa da ƙarfafa hanyoyin tara kuɗaɗen shiga, rage gibin kasafin kuɗi da kuma aiwatar da manufofin da za su taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasa a nan gaba.
