Saurari premier Radio
24.5 C
Kano
Sunday, September 8, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiKisan Hanifa: Abdulmalik ya musanta kasheta a Kotu

Kisan Hanifa: Abdulmalik ya musanta kasheta a Kotu

Date:

Abubakar Haruna Galadanci

A yayin da aka ci gaba da zaman kotun kan shari’ar kisan kan da aka yiwa hanifa, wanda ake zargi da kisan ya musanta aikata hakan a gaban kotu.

A zaman kotun na yau Litinin karkashin mai shari’a Usman Na’abba, Abdulmalik Tanko ya ce kokadan ba shi ya kasheta ba kuma bashi da masaniya kan aikata hakan.

Idan za a iya tunawa dai Abdulmalik ya amsa kisan Hanifa bayan da rundunar ‘yan sanda ta yi holinsa a shalkwatarsu.

Har ma ya bayyana cewar ya kasheta ne da shinkafar bera ta N100 bayan da ya saceta ya kuma boyeta a wani wuri.

Sai dai bayan da aka gurfanar da shi a gaban babbar kotun jiha ranar litinin ya ce ko kadan bai aikata kisan kanba.

Wannan ce ta sanya alkalin kotun ya dage shari’ar har zuwa ranar 2 da 3 ga Maris mai kamawa domin sauraron karar, ya kuma bayar da umarnin a ci gaba da tsareshi a gidan yari.

Latest stories

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye muƙaminsa

Mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan...

Related stories

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye muƙaminsa

Mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan...