25.9 C
Kano
Sunday, June 4, 2023
HomeLabaraiKasuwanciJirgin Qatar ya fara suka a Kano

Jirgin Qatar ya fara suka a Kano

Date:

Related stories

Maniyyata 17,000 ne suka bar Najeriya zuwa kasa maitsarki-NAHCON

Bayan kwashe kwanaki bakwai da fara jigilar alhazan Najeriya...

Mukhtar Yahya Usman

Kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Qatar Airways ya fara sauka a birnin Kano  a yau Laraba.

 Jirgin ya sauka cikin murna da annashuwa daga hukumomin ƙasar  nan da kuma kamfanin.

Jirgin Boeing 787 ya sauka a babban filin jirgi na Mallam Aminu Kano (MAKIA) da misalin ƙarfe 11:00 da ɗoriya.

Jekadan Najeriya a ƙasar Qatar, wadda ta mallaki kamfanin, Ahmadu Yakubu Abdullahi na cikin waɗanda suka halarci bikin saukar jirgin karon farko a tarihi.

Kano ce wuri na uku a kasar nan da kamfanin zai dinga sauka bayan Abuja da Legas.

A gobe Alhamis kuma zai ƙarasa birnin Fatakwal na Jihar Rivers.

Latest stories