Saurari premier Radio
26.9 C
Kano
Wednesday, May 1, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnatin KanoHukumar yaki da cin hanci ta Kano ta bada belin darakta a...

Hukumar yaki da cin hanci ta Kano ta bada belin darakta a hukumar kare hakkin mai siyan kayayyaki

Date:

Hukumar yakin da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta bayar da belin daraktan tabbatar da nagartar kayyaki a hukumar kare hakkin mai sayen kaya ta jihar Kano Malam Bello Alkarya .

Shugaban hukumar Barrister Mahmud Balarabe ne ya bayyana hakan a zantawarsa da Premier Radio ranar Asabar.

Barrister Mahmud ya ce an bayar da belinsa ne sakamakon rashin lafiya da yake fama da ita, bayan ya kwashe kwanaki biyu a hukumar.

“An bayar da belinsa sakamakon rashin lafiyar da yake fama da ita.

“Kuma za a dawo da shi ranar Litinin mai zuwa domin ci gaba da tuhumar da ake yi masa.” A cewarsa.

Hukumar ta kama Alkarya ne a ranar Alhamis din da ta gabata bisa zargin cinhanci da rashawa.

Ko a watannin baya sai da aka kama wani daraktan hukumar da makamancin wannan zargi.

A makon da ya gabata ma sai da hukumar tsaro ta DSS ta tsare shugaban hukumar Janar Idris Bello Dambazau, kan zargin rufe wasu gidajan mai a nan Kano ba bisa ka’ida ba.

A yan kwanakin nan dai mutuncin hukumar na ta zubewa a idon jama’a la’akari da yadda ake ta samun manyanta da laifukan almundahana da kudaden al’umma.

Latest stories

Netanyahu ya nanata ƙudirin sojojin Isra’ila na kai farmaki ta ƙasa a Rafah.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nanata kudirin sojojin Isra'ila...

NiMet ta yi hasashen samun mamakon ruwan sama a wasu jihohin.

Wani has ashen hukumar Kula da Yanayi ta kasa...

Related stories

Netanyahu ya nanata ƙudirin sojojin Isra’ila na kai farmaki ta ƙasa a Rafah.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nanata kudirin sojojin Isra'ila...

NiMet ta yi hasashen samun mamakon ruwan sama a wasu jihohin.

Wani has ashen hukumar Kula da Yanayi ta kasa...