Mukhtar Yahya Usman
Asibitin Kashi na Dala ya bayyana aniyarsa na yiwa wadanda harin jirgin kasan Kaduna-Abuja ya rutsa da su magani kyauta.
Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan gudanarwa na asibitin. Mal. N Harazumi ya sawa hannu.
Harazumi yace aikin zai kasance ne karkashin umarnin ma’aikatar lafiya ta kasa.
Sanarwar da aka aikewa dukkanin shugabannin bangarorin asibitin ta bukaci su yiwa duk wanda aka kawo bangarensu aiki kyauta.
Idan za a iya tunawa a ranar 28 ga Maris me yan ta’adda suka sanya bom akan hayar titin Jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja da yayi sanadiyyar hallaka da jikkata mutane da dama.