Saurari premier Radio
39.9 C
Kano
Wednesday, April 24, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiAddiniHaramcin amfani da mutum-mutumi a Kano na nan daram – Hisbah

Haramcin amfani da mutum-mutumi a Kano na nan daram – Hisbah

Date:

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta ce har yanzu haramcin da ta sanya kan amfani da mutum-mutumi a shagunan sayar da kayan sawa da na teloli a fadin Jihar na nan daram.

A watan Yunin bara ne dai hukumar ta sanar da haramta amfani da mutum-mutumin a Jihar, tare da barazanar kama duk wanda ya karya dokar.

A cewar Babban Kwamandan hukumar, Harun Ibn Sina, sun dauki matakin ne saboda amfani da mutum-mutumin ya saba da koyarwar addinin Musulunci.

Sai dai a wani taro da ta yi da Kungiyar Teloli ta Kasa reshen Jihar ranar Alhamis, hukumar ta Hisbah ta sake jaddada cewa haramcin na nan daram.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sashen yada labarai na hukumar ya fitar a ranar Juma’a.

A cewar Ibn Sina yayin taron nasa da telolin “Hukumar Hisba ta Jihar Kano bisa dogaro da sashen dokar Hisba ta shekarar 2001, wacce aka yi wa kwaskwarima a 2003, ta hana kowanne mai dinki saka mutum-mutumi, wanda yake dauke da siffar mutum cikakkiya, ko ta mace ko ta namiji.

“Amma za a iya anfani da wanda babu kai ajikinsa ko a jikanta, ita ’yar tsanar da ake saka wa kaya.

“Wannan shine kadan daka cikin muhimman abin da aka tattauna a kai yau,” inji Ibn Sina.

Daga nan sai Kwamandan na Hisbah ya yi kira ga telolin da su bi dokar ta hukumar tare da neman su tsaftace sana’ar tasu.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...