wamnan Sakkwato, Ahmad Aliyu, ya kara wa’adin mulki ga shugabannin ƙananan hukumomin jihar su 23.
Gwamnan ya kara musu wa’adin ne kamar yadda dokar kananan hukumomi da aka yi wa gyaran fuska ta 2008 ta ba da dama.
Karin wa’adin zai bai wa hukumar zaben jiha damar shirya zaben shugabanni kananan hukumomi 23 da na kansilolinsu 244.
Sakataren yada labaran gwamnan, Abubakar Bawa, a bayanin da ya fitar, ya ce gwamnan ya taya murna ga shugabannin rikon kan karin wa’adin.
Ya ba su tabbacin ci gaba da goya musu baya su saukar da nauyin da aka dora musu.