EFCC ta bukaci Daractan kudi na hukumar da Muhuyi ke jagoranta ya bayyana a Abuja don gabatar da bayanan kudaden da suka shiga ofishin Muhuyi Magaji Rimin Gado daga 2019 zuwa 2021.
Binciken EFCC kan Muhuyi na zuwane yayin da shima ya kaddamar da bincike kan bidiyon Dala da hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci a Kano ke zargin tsohon gwamnan Kano kuma shugaban APC na kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje.