Mai martaba sarkin Kano Alh Aminu Ado Bayaro ya bukaci masu hannu da shuni da su dinga koyi da kungiyoyin kishin alumma wajen kayawa matasa sana’a.
Sarkin ya ya bukaci hakan yayin yaye dalibai mata da Gidauniyar El’s Foundation ta koyar a kofar Kudu.
Sarkin ya buka masu hannu da shuni suyi koyi da irin wannan tsari da kungiyar tayi na taimakawa matasa da yan mata.
A nata jawabin shugabar kungiyar Amb Adesuwa Udo ta ce ta koyar da matasa da yan mata sana’o’in hada takalmi jaka dinki manshafawa da dai sauran sanaoin daban daban.
mai martaba sarkin ya kuma karbi bakonci mai martaba sarkin Tangale Alhaji Muhammadu Danladi Sunusi a fadarsa jim kadan bayan kammala taron