Mukhtar Yahya Usman
Zabe Jam’iyyar APC ta ce ta shirya tsaf domin soma gangamin yakin neman zabenta na 2023.
Gwamnan Filato Simon Lalong ne ya bayayana hakan ga manema Labarai a Abuja.
Lalong wanda shi ne shugaban gangamin yakin neman zaben shugaban kasa ya bayyana hakan bayan kammala sa ido kan gyara ofishin gangamin yakin neman zabensu da ke Abuja.
Gwamnan ya kuma gana da wasu ma’aikatan kwamitin yakin neman zaben, a kokarin tabbatar da cewa komai ya tafi daidai.
Ya kuma samu ganawa da ɗan takarar shugabancin kasa, Asiwaju Bola Tinubu, a hedikwatar.