Saurari premier Radio
28.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiMasu zanga-zanga sun hana shari'ar Mua'az Magaji

Masu zanga-zanga sun hana shari’ar Mua’az Magaji

Date:

Masu zanga-zanga sun kawo wa zaman kotu cikas yayin da take ƙoƙarin ci gaba da sauraron ƙarar Mu’azu Magaji (Win Win) kan zargin cin zarafin Gwamna Ganduje da iyalansa.

Jami’an kotun da ke Nomans Land, Sabon Gari a nan Kano na cewa ba za su fara sauraron ƙarar ba har sai ‘yan zanga-zangar sun bar wurin.

Matasa ɗauke da kwalaye da ke nuna goyon baya ga tsohon kwamashinan na ayyuka sun yi cincirundo a bakin kotun, inda suke nema asaki Mu’azu Magajin.

A cewarsu tsare Ma’azu Magaji tamakar tauye masa hakkinsa ne da ya kamata a ce yana sararawa a cikin jama’a.

A wani bangaren kuma wasu matasan ne sauke da kwalaye da ke nuna bukatar a hukuntashi.

Matasan dai da suka yi ikirarin cewa su dalibai ne sun ce ba za su amince da cin zarafin gwamnan da Dansarauniya ke yi ba.

A don hakan ne ma suke bukatar kotu da ta tabbatar ta hukunta shi domi ya zama izina ga yan gaba.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...