Janhoriyar Gambiya ta bukaci gwamnatin Nigeria data ba daliban kasar ta tallafin karatu a jami’oin kasar nan.
Ministan ilimi da kimiyar zamani farfesa Pieme Gomez, yayi wannan rokon alokacin da yakaiwa Mai rukon mukamin Sakataren hukumar kula da jami’oin (NUC) Chris Maiyaki a Abuja.
Farfesa Gomez, ya yabawa Nigeria a game da kafa jami’ar ilimi a Gambiya, Wanda ya hada da manyan malamai da Kuma mataimakin shugaban jami’ar na farko Wanda dan Nigeria ne.
Yace Gambiya tana da matukar sha’awar ganin ansamarwa masu karatun digiri na biyu a fannin Kimiya, fasahar zamani, Fannin kere kere, da Kuma Lissafi.
A jawabin sa babban Sakataren NUC na ruko Chris Maiyaki, ya baiwa ministan tabbacin samun goyon bayan Nigeria duk da nata matsalolin da take fuskanta.