Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiIndependence: Buhari zai yiwa alummar kasa jawabi

Independence: Buhari zai yiwa alummar kasa jawabi

Date:

Ana sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai yiwa alummar kasar nan jawabi da safiyar ranar Asabar.

Wanann na zuwa ne a Wani bangare na bikin samun ‘yancin-kan Najeriya shekaru 62.

Muhammadu Buhari zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi ranar Asabar, 1 ga watan Oktoba.

Buhari zai gudanar da jawabi ne da misalin ƙarfe 7:00 na safe yayin da Najeriya ke cika shekara 62 da samun ‘yancin-kai daga Turawan Birtaniya.

“Ana umartar gidajen talabijin da rediyo da sauran kafofin labarai na latironi da su jona jawabin daga gidan talabijin na NTA da kuma Rediyo Najeriya,” a cewar wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasar.

Tun daga farkon makon nan aka ga sojojin Najeriya na shirye-shiryen bikin na ranar Asabar, inda jiragen soja za su dinga wasa a sama da kuma faretin girmamawa.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...