Saurari premier Radio
38.9 C
Kano
Saturday, April 20, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiHukumar jin dadin alhazai ta baiwa maniyyata mako guda su cika kudadensu

Hukumar jin dadin alhazai ta baiwa maniyyata mako guda su cika kudadensu

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Hukumar Jin dadin alhazai ta jihar Kano ta baiwa maniyyatan da suka biya wani bangare na kudaden aikin hajjin bana wa’adin mako guda su cika kudadensu.

Babban sakataren hukumar Alhaji Muhammad Abba Danbatta ne yayi wannan bayanin yayin taron manema Labarai ranar Alhamis.

Ya ce za a rufe karbar kudin daga ranar Juma’a 12 ga Maris din da muke ciki.

Haka kuma ya ce hukumar ba za ta sake bayar da wata dama ba idan maniyyata suka gaza biyan kudaden bayan cikar wa’adin.

Babban sakataren ya kuma bukaci wadanda shekarunsu suka haura 65 da su je hukumar domin karbar kudadensu.

Idan za a iya tunawa dai tuni hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON ta baiwa jihar Kano adadin kujera 2229.

Sai dai adadin wadanda suka biya kudin ajiya tun a shekarar 2019 sun zarta adadin kujerun Kano.

Wannan ce ta sanya hukumar ke bukatar duk wanda ke bukatar zuwa aikin hajjin a bana da ya gaggauta cika kudinsa kafin cikar wa’adin.

Wannan ne dai zai baiwa hukumar damar baiwa masu son biyan kudin aikin hajjin a bana, idan masu ajiya basu cika ba.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...