Saurari premier Radio
25.6 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnatin jihar Kebbi ta raba kayan agaji ga mutane wadanda bala’in ambaliyar...

Gwamnatin jihar Kebbi ta raba kayan agaji ga mutane wadanda bala’in ambaliyar ruwa ya shafa a jihar a bara

Date:

Gwamnatin jihar Kebbi ta raba kayan agaji ga mutane 9,100 wadanda bala’in ambaliyar ruwa ya shafa a jihar a bara.
Jimillar mutane 22,202 ne za su gajiyar callafin daga kashi na farko da na biyu da kuma na uku.
Gwamna Nasir Idris a lokacin da yake jawabi a wajen raba tallafin kashi na farko ya sanar da kafa kwamitin da zai tabbatar da cewa kayayyakin sun isa ga wadanda aka yi niyya a kowace karamar hukumar jihar.
Gwamnan wanda mataimakinsa Sanata Umar Abubakar Tafidan Kabi ya wakilta ya ce kowane kwamiti zai kasance karkashin jagorancin kwamishina a karamar hukumar ko kuma mai ba shi shawara na musamman.
Tun da farko a nasa jawabin babban daraktan hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA, Alhaji Mustapha Habib Ahmed wanda ya samu wakilcin Alhaji Ibrahim Yusuf ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta amince da daukar matakin musamman ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa bara.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...