Jami’an Amurka da Iran sun fara tattaunawa a ƙasar Oman, yayin da Washington ke ƙoƙarin daƙile shirin nukiliyar Tehran.
Tattaunawar na gudana ne ta hannun shiga-tsakani, inda jami’an diflomasiyyar Oman ke taimakawa wajen haɗa ɓangarorin biyu.
Ministan harkokin wajen Oman ya bayyana cewa tattaunawar ta fi karkata ne kan shiryawa da tsara ƙa’idojin da za a sanya domin ci gaba da yarjejeniyar.
A nata ɓangaren, Iran ta ce har yanzu tana da shirin ci gaba da tattaunawa kan shirinta na nukiliya, amma ta jaddada cewa ba za ta amince a tattauna batun makamanta masu linzami ba.
Sai dai kuma Amurka ta riga ta girke sojoji a gaɓar Iran, tare da yin barazanar kai hari, idan Tehran ba ta haƙura da wasu manya-manyan abubuwa ba.
