Saurari premier Radio
22.3 C
Kano
Tuesday, September 24, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiMajalisar dattijai za ta tantance sabon gwamnan CBN Dr Olayemi Cardoso

Majalisar dattijai za ta tantance sabon gwamnan CBN Dr Olayemi Cardoso

Date:

Majalisar dattijai za ta tantance sabon gwamnan bankin kasa da shugaban kasa Bola Tinubu ya nada Dr Olayemi Cardoso domin tabbatar da nagartar sa kafin sahale masa hawa kujerar gwamnan babban bankin.

Haka zalika mataimakan gwamnan 4 da shugban kasa ya nada, zasu bayyana gaban majalisar a yau Talata domin tantancewa, kafin su sami sahalewar jagorantar al’amuran bankin zuwa shekaru 5 nan gaba.

Dr Cordoso dai tsohon kwamishinan kasafi da tsare tsaren tattalin arziki ne lokacin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu a jihar Lagos.

Majalisar dattijan zata dawo aiki bayan dogon hutun watanni biyu, da shirin tantance karin sabbin ministoci 2 da shugaban kasa ya aike mata, a ranar talata 3 ga watan oktoba mai kamawa.

Idan za a iya tunawa dai shugaba Tinubu ya nada Dr Jamila Ibrahim da Ayodele Olawande a matsayin ministoci yayin da majalisar ke hutu

Latest stories

Related stories

Tinubu ya gana da Sarki Charles III a fadar Buckingham

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri...

PDP ta ki sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a zaben gwamnan jihar Edo

Jam’iyyar PDP ta ki sanya hannu kan yarjejeniyar zaman...