Gwamnatin Jihar Filato da ke arewacin Nijeriya ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun firamare da sakandare na gwamnati da masu zaman kansu na wucin-gadi.
Hakan na zuwa ne a cikin wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar a ƙarshen mako a matsayin wani mataki na kariya daga waɗanda ake zargi sun kamu da cutar mashaƙo (diphtheria).
Sanarwar wadda Kwamishinar Yada Labarai ta jihar, Joyce Ramnap ta fitar ta bayyana cewa, rufe makarantun zai soma aiki ne daga ranar Litinin, 7 ga watan Satumba har zuwa lokacin da gwamnati za ta sake fitar da “sanarwar buɗe makarantun.’’
Kazalika Kwamishinar ta bayyana cewa rufe makarantun ya shafi dukkan makarantu, ciki har da waɗanda suka riga suka koma aiki a sabon zangon karatu na shekarar 2026 zuwa 2027.
Haka kuma an yi kira ga iyaye da malamai da kuma hukumomin makarantu da su bi wannan umarni da aka bayar.
Matakin rufe makarantun ya zo ne a daidai lokacin da ake ƙara nuna damuwa game da fargabar ɓarkewar cutar mashaƙo a jihar.
