Hukumar kula da yanayi ta kasa NiMet, ta yi gargaɗin samun ambaliya a a nan jihar Kano da mama wasu jihohin ƙasar nan sakamakon mamakon ruwan sama da za a samu kwanan nan.
Hukumar ta ce jihohin da suka haÉ—a da Kano, da Katsina, da Zamfara, da Jigawa da Kebbi da Kaduna, da kuma jihar Adamawa na cikin barazanar fuskantar ambaliyar ruwa, don haka ne ta yi kira ga mahukuntan jihohin su É—auki matakan kare al’ummominsu.
Tuni dai dama ambaliyar ta fara É“arna a wasu jihohin Najeriya inda aka samu asarar rayuka da ta dukiyoyi.
Alhaji Bashir Idris Garga, darakta a hukumar bada agajin gaggawa ta Najeriyar NEMA ya ce wannan ruwan saman da za ayi na kwana uku ba ƙaƙautawa zai sanya magudanar ruwa da dama ba a cika damuwa da yashe su ba su cike wanda daga bisani ruwan zai malala har ya je yayi ɓarna.