Ministan Gidaje da ci gaban birane, Ahmed Musa Dangiwa, ya nuna rashin jin dadinsa kan yadda aikin gina gidaje 500 ke tafiya a nan jihar Kano.
Ahmad Dangiwa ya bayyana rashin jin dadinsa ne a lokacin da ya kai ziyarar duba yadda aikin ke gudana a karshen mako.
Ya kuma ce matuka aikin ba ya sauri kamar yadda aka tsara tun da fari zai gudana.
Ma’aikatar Gidaje da ci gaban birane ta kasa ce dai ta fara gina gidaje 500 a Jihar Kano, a wani yunkuri na gina sabbin muhali ga masu bukata.
Aikin ginin gidajen wanda aka yi wa lakabi da Renewed Hope Estate na gudana ne wani a kauye dake Lambu a karamar hukumar Tofa a arewacin Kano.
Aikin ya haÉ—a da gina gida mai É—aki biyu, É—aki É—aya, da kuma waÉ—anda ke da É—aki uku.
Ya gargadi wadanda aka bai wa aikin gina gidajen da ya hanzarta ko kuma gwamnati ta kwace aikin daga hannusa.
Sai dai wanda aka bai wa kwantiragin aikin wanda manajan kamfanin Haruna Lawal ya wakilta, ya gayawa ministan tabbacin za su kara himma don ganin aikin ya kammala kafin cikar wa’adin da aka debar musu.