Aminu Abdullahi Ibrahim
Sanata Rabi’u Kwankwaso ya bayyana takaicin sa kan yadda aka tsalleke gwamnatin Kano cikin gwamnonin jihohi 35 da aka rabawa tallafin shinkafa.
Tsohon gwamnan na Kano ya bayyana hakane a shafukan sa na sada zumunta a ranar Litinin.
Kwankwaso, ya ce an mika kason Kano hannun APC maimakon yadda aka baiwa kowane gwamna.
Ya ce wannan cin fuska ne ga kundin tsarin mulki na Dimukuradiya da nuna bangaranci na jam’iya.
Yayi kira ga shugaban kasa Tinubu da ya gaggauta dakatar da wannan dambarwa dake neman tintsirar da Dimukuradiya.
Sanata Kwankwaso ya kuma bayyana takaicin sa dangane da yadda aka sauya daraktocin DSS uku a Kano cikin makonni 2.
Ya ce wannan sauye sauye na shafar tsaron jihar Kano.