Babbar kotun tarayya a Abuja ta sahalewa hukumar nan ta EFCC mai yaki da masu yiwa tattalin arziki zagon kasa ta rufe asusun kirifto na wasu mutane hudu.
Maishari’a Emeka Nwite, ya amincewa hukumar ta rufe asusun bisa zargin karya dokar kasa.
EFCC na zargin masu asusun da daukar nauyin ta’addanci, da halasta kudin haram, da daukar nauyin zanga-zanga a kasar nan.
Kotu ta ba hukumar EFCC damar kulle asusun kirifto da ke dauke da kudi Dala milyan talatin da bakwai, kamar yadda majiyarmu ta tabbatar.