Mutanen da suka rasu sanadyiyar ambaliyar ruwa a jihar Jigawa sun karu zuwa talatin, yayin da gonaki fiye da kadada dubu tara suka lalace, tare da rushewar gidaje fiye da dubu hudu.
A iya cewa ambaliyar bana ta bambanta da aka saba gani duk da sanin cewa hukumar kula da yanayi ta kasa tayi hasashen Jigawa na daga cikin jihohin da zasu fuskanci ambaliya a bana.
A yanzu dai fiye da yankunan jihar casa’in ne suka fuskanci ambaliyar, yayin da shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar, Haruna Mairiga, ya ce gwamnati zata taimakawa wadanda iftila’in ya shafa da buhunan shinkafa da gero da gari da magunguna.
Ya ce suna aiki ba-dare-ba-rana domin tallafawa wadanda abun ya shafa.