Gwamnatin Jihar ta rufe wani gidan marayu da ke birnin Ilorin, bayan gano cewa cibiyar tana gudanar da ayyukanta ba tare da samun izinin da ya dace ba.
Hukumomin jihar sun kuma ceto yara 30 da ke cikin gidan, yayin da ake ci gaba da daukar matakan da suka dace domin tabbatar da tsaron lafiyarsu da jin dadinsu.
Rahotanni sun ce hukumomin jihar sun ɗauki matakin ne bayan gano cewa gidan marayun yana gudanar da ayyukansa ba tare da amincewar gwamnati ba.
An kwashe yaran daga wurin domin tabbatar da tsaronsu da jin daɗinsu.
Gwamnatin jihar ta ce za ta ci gaba da sanya ido kan cibiyoyin kula da yara, tare da ɗaukar matakan da suka dace kan wuraren da ke gudanar da irin wannan aiki ba tare da bin ƙa’idojin gwamnati ba.
