Saurari premier Radio
24.8 C
Kano
Sunday, September 22, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnan Kano ya nada sabbin shugabannin Kano Pillars

Gwamnan Kano ya nada sabbin shugabannin Kano Pillars

Date:

Gwamnan Kano ya nada sabbin shugabannin Kano Pillars

Ahmad Hamisu Gwale 

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya nada sabbin shugabanin hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars.

 

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Lahadi, yace Abba Yusuf ya amincewa da nadin sune bayan karewar wa’adin tsaffin Shugabannnin.

 

A watan da muke ciki ne dai aka sallami Babangida Umar Little daga jagorancin kungiyar da ake yiwa take da sai masu gida.

 

Ofishin kwamishinan matasa da wasanni, Mustapha Rabiu Kwankwaso ya sanar da cewa an nada mutum 14 da za su ja ragamar Pillars a matakai daban-daban.

 

Tuni dai aka nada Ali Na Yara mai Samba a sabon shugaban kungiyar a mataki na rikon kwarya na shekara daya tare da karin mutum 12 har da Abubakar Isa Dandago a matakin jami’in yada labaran kungiyar.

 

Sanarwar ta bayyana sabbin shugabannin za su yi aiki tare da ma’aikatar matasa da wasanni ta jihar da sauran masu ruwa da tsaki domin kai Pillars gaba..

 

Jerin shugabannin Kano Pillars sun hadar da

 

Aliyu Nayara Mai Samba – Shugaba

 

Salisu Muhammad Kosawa – Mamba

 

Abubakar Isa Dandago – Jami’in yada labarai

 

Ismail Abba Tangalash- Mataimakin Jami’in yada labarai

 

Yusuf Danladi Andy Cole – Mamba

 

Muhammad Usman – Mamba

 

Ahmad Musbahu – Mamba

 

Umar Umar Dankura – Mamba

 

Rabiu Abdullahi – Mamba

 

Nasiru Bello- Mamba

 

Muhammad Danjuma Gwarzo – Mamba

 

Mustapha Usman Darma – Mamba

 

Muhammad Ibrahim (Hassan West) – mamba

 

Engr Usman K/Naisa- Mamba.

 

Haka zalika gwamnan ya nada kaftin É—in Najeriya (Super Eagles) Ahmed Musa, a matsayin jakadan wasanni na jihar Kano.

 

Tuni dai ake saran fara gasar gasar Firimiyar Najeriya ta kakar wasannin shekarar 2024/2025 daga 31 ga watan Agusta.

 

Kuma hukumar shirya gasar ta NPFL ta tanadi naira miliyan 200 ga duk kungiyar data lashe gasar Firimiyar Najeriya.

Latest stories

Related stories

Tinubu ya gana da Sarki Charles III a fadar Buckingham

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri...

PDP ta ki sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a zaben gwamnan jihar Edo

Jam’iyyar PDP ta ki sanya hannu kan yarjejeniyar zaman...