Fadar shugaban kasa ta karyata zargin da ake na cewa an samu wata baraka tsakanin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima.
Mai magana da yawun mataimakin shugaban kasa Stanley Nkwocha ne ya sanar da hakan cikin sanarwar taya Kashim Shettima murnar cika shekaru 58 a duniya.
Nkwocha ya bayyana ikirarin rashin jituwa a tsakanin shugabannin biyu a matsayin karya, inda ya jaddada cewa mataimakin shugaban kasa mutum ne mai biyayya ne ga shugaba Tinubu, sannan yana da alaka mai kyau da sauran manyan jami’an gwamnati.
Ya kara da cewa zargin ya fito ne daga wajen wasu makiya ci gaban Najeriya, da suke son kawo rudani don kawar da hankalin al’umma daga ayyukan raya kasa da gwamnatin tarayya ke yi a sassa daban daban na kasar.