Saurari premier Radio
24.8 C
Kano
Sunday, September 22, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiDuk da ikirarin habaka noma gwamnatoci sun yi biris da manoma -...

Duk da ikirarin habaka noma gwamnatoci sun yi biris da manoma – AFAN

Date:

Manoma sun fara korafi game da yadda gwamnatocin kasar nan suka yi biris da al’amuransu, duk da ikirarin da su ke yi nayin bakin kokari domin kara habaka fannin noma.

Sun ce a yanayin da ake ciki na damuna, har yanzu wasu gwamnatoci ba su taimaka musu da kayan aikin gona ba.

Shugaban gamayyar kungiyoyin manoma ta kasa AFAN reshen jihar Kano, Abdullahi Ali Maiburodi, ya ce tun cikin watan Afrilu suke nusar da gwamnati da masu fada aji game da hanyoyin inganta samun wadataccen abinci, musamman a wannan lokaci da ake fama da tashin farashin kayan masarufi.

Abdullahi Maiburodi, ya ce bana dai ba su samu komai daga dukkan bangarori na tallafi ba, saboda haka suke kara kira a taimaka musu.

Korafin manoman na zuwa ne yayin da a kwanakin baya gwamnatin Kano ta sanar da yin rabon taki ga manoma a yankunan kananan hukumomin jihar 44.

Latest stories

Related stories

Tinubu ya gana da Sarki Charles III a fadar Buckingham

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri...

PDP ta ki sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a zaben gwamnan jihar Edo

Jam’iyyar PDP ta ki sanya hannu kan yarjejeniyar zaman...