Kotun ƙoli ta jinkirta yanke hukunci kan ƙarar da Atiku Abubakar ya shigar gabanta yana ƙalubalantar nasara da Bola Tinubu ya samu a zaben 2023 .
Bayan jin ta bakin kowane ɓangare, Lauyan Atiku Abubakar Chris Uche SAN da Lauyan Hukumar Zaɓe Abubakar Mahmoud SAN da Lauyan Bola Tinubu Wole Olanipekun da kuma Lauyan Jamiyyar APC Akin Olujinmi, alƙalan sun yanke Shawarar jinkirta yanke hukunci kan batun.
Haka nan kotun ta saurari bahasi daga kowane bangare kan yunƙuri ɗan takarar PDP Atiku Abubakar na gabatar da sabbin shaidu gaban kotun.