Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa yaƙin da ƙasarsa ke yi da Iran na iya karewa cikin “gaggawa”, yayin da ya kare matakan soji da Amurka da Isra’ila suka ɗauka a kan Iran.
Trump ya faɗi hakan ne yayin da yake magana da ‘yan majalisar Jam’iyyar Republican a wani jawabi da ya gabatar, inda ya bayyana cewa farmakin sojin Amurka ya samu gagarumar nasara.
A ranar 28 ga Fabrairu, 2026, Amurka da Isra’ila suka kaddamar da manyan hare-haren sama da na makamai masu linzami kan wasu muhimman cibiyoyin sojin Iran.
Hare-haren sun fada kan tsarin kariyar sararin samaniyar Iran, wuraren harba makamai masu linzami, da kuma wasu kadarorin rundunar ruwan Iran.
Hare-haren na ranar farko sun yi sanadin mutuwar jagoran addinin Iran a wancan lokaci, Ayatollah Ali Khamenei.
Trump ya bayyana wannan farmaki a matsayin wani “gajeren aiki na soja”, yana mai cewa Amurka ta shiga ne domin dakile abin da ya kira “mugunta”.
Ya ce ƙwarewar sojojin Amurka za ta sa rikicin ya kasance na ɗan lokaci kaɗan.
A cewarsa, rundunar sojin Amurka ta riga ta lalata kusan kashi 80 cikin 100 na na’urorin harba makamai masu linzami na Iran, wanda ya rage ƙarfin Iran sosai.
Ya ce:
- An lalata yawancin makamai masu linzami na Iran
- An ragargaza jiragen yaki marasa matuka (drones)
- Ana kai hare-hare kan wuraren da ake kera drones
Trump ya kuma yi ikirarin cewa sojojin Amurka sun nutsar da jiragen ruwan yaki 46 na Iran cikin kwanaki uku da rabi.
Trump ya ce Amurka ta kai harin ne saboda zargin cewa Iran na shirin kai hari kan Amurka da kawayenta cikin mako guda.
Sai dai har yanzu gwamnatin Amurka ba ta gabatar da hujjoji a bainar jama’a da ke tabbatar da wannan zargi ba.
Ya kara da cewa Iran ta nufi wasu ƙasashen Gabas ta Tsakiya da makamai, ciki har da:
- Qatar
- Saudi Arabia
- United Arab Emirates
Trump ya yi murna da kashe wasu manyan shugabannin Iran, yana mai cewa yanzu ba a san wa zai jagoranci ƙasar ba.
Ya kuma danganta lamarin da harin da Amurka ta kai a wa’adinsa na farko wanda ya kashe Janar Qassem Soleimani, tsohon kwamandan rundunar IRGC Quds Force.
Bayan mutuwar Ali Khamenei, Iran ta nada ɗansa Mojtaba Khamenei a matsayin sabon jagoran ƙasar.
Trump ya ce bai gamsu da wannan mataki ba, yana mai cewa hakan na iya haifar da ci gaba da matsaloli a Iran.
Sai dai ya ƙi bayyana ko sabon jagoran na cikin jerin mutanen da za a iya kai wa hari a nan gaba.
Trump ya ce duk da nasarorin da Amurka ta samu a yaƙin, har yanzu ana buƙatar ƙarin matakai.
“Mun riga mun yi nasara ta hanyoyi da dama, amma har yanzu ba mu yi nasara cikakke ba,” in ji shi.
