Gwamnatin Jihar Nasarawa, karkashin hadakar da ta kulla da gwamnatin tarayya, ta fara rabar da takin zamani 74,800, a daukacin fadin jihar.
Har ila yau, ta yi hakan ne domin kara bunkasa yin girbin amfanin gona a jihar.
Kowane manomi daya, zai samu Buhu daya, inda aka ware Buhununa guda 500, domin a raba wa manoman da aka zabo daga mazabu 147, sai kuma Buhuhuna guda 100 za a rabar a kananan hukumomi 13 na jihar.
A jawabinsa a wajen taron rabar da takin a garin Lafia, gwamnan jihar Abdullahi Sule ya bayyana cewa; yana da yakinin cewa; manoman da suka amfana da takin za su yi amfani da shi, domin kara habaka aikin noma a fadin jihar.
Gwamna Sule, ya kuma gargadi wadanda aka dora wa nauyin rabar da takin, kan karkatar da takin; wanda ya sanar da cewa, gwamnatinsa ba za ta lamunta ba.
